Thursday, 5 January 2017

kungiyar 'yan asalin yankin Biafara (IPOB) ta yi gargadi game da Buhari

- IPOB ta ce shugabancin Buhari na kama karya zai ruguza Najeriya.
- Kungiyar mai goyon bayan kafa kasar Biafara ta yi gargadi cewa mummunan rikici na dab da faruwa a Najeriya
kungiyar 'yan asalin yankin Biafara (IPOB) ta yi gargadi game da Buhari
kungiyar 'yan asalin yankin Biafara (IPOB) ta yi gargadi game da Buhari
Kungiyar ta ce Najeriya ka iya fuskantar tashin hankali sanadiyyar salon mulkin kama karya na shugaba Muhammadu Buhari, su na masu bayar da misali da kin sakin shugabansu Nnamdi Kanu daga tsarewar da a ke masa.
Vanguard ta rawaito cewa hakan na dauke ne a wata sanarwa da Sakataren yada labaran kungiyar, Comrade Emma Powerful ya sanya wa hannu, a ranar Talata 3 ga watan Janairu.
Powerful ya kuma ce sakin fefayen bidiyo na tonon asirin abubuwan da a ke ba dai-dai ba a kasar nan zai ci gaba da bankado gaskiyar da a ke boyewa wadanda ka iya rusa Najeriya kamar yadda Nnamdi Kanu ya yi barazana.

No comments:

Post a Comment