- IPOB ta ce shugabancin Buhari na kama karya zai ruguza Najeriya. 
- Kungiyar mai goyon bayan kafa kasar Biafara ta yi gargadi cewa mummunan rikici na dab da faruwa a Najeriya

kungiyar 'yan asalin yankin Biafara (IPOB) ta yi gargadi game da Buhari
Kungiyar
 ta ce Najeriya ka iya fuskantar tashin hankali sanadiyyar salon mulkin 
kama karya na shugaba Muhammadu Buhari, su na masu bayar da misali da 
kin sakin shugabansu Nnamdi Kanu daga tsarewar da a ke masa.
Vanguard
 ta rawaito cewa hakan na dauke ne a wata sanarwa da Sakataren yada 
labaran kungiyar, Comrade Emma Powerful ya sanya wa hannu, a ranar 
Talata 3 ga watan Janairu.
Powerful ya kuma ce 
sakin fefayen bidiyo na tonon asirin abubuwan da a ke ba dai-dai ba a 
kasar nan zai ci gaba da bankado gaskiyar da a ke boyewa wadanda ka iya 
rusa Najeriya kamar yadda Nnamdi Kanu ya yi barazana.
 
No comments:
Post a Comment